in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun Isra'ila sun kai hari kan sansanin kungiyar Hamas dake Gaza
2017-12-08 11:22:53 cri
Motar yakin dakarun Isra'ila, ta harba ababen fashewa 2 zuwa sansanin soji a zirin Gaza, sai dai babu wanda ya ji rauni.

Kafar yada labaran Isra'ila ta ce an kai harin ne sansanin kungiyar Hamas dake gabas da sansanin 'yan gudun hijira na al-Mughazi dake tsakiyar zirin Gaza, a wani mataki na mayar da martani ga rokokin da aka harba daga Gaza zuwa yankin kudancin Isra'ila.

Majiyoyi daga jami'an tsaron Falasdinu na cewa, motocin yakin Isra'ila 2 sun harba ababen fashewa zuwa sansanin soji dake tsakiyar Zirin Gaza, inda suka ce babu wanda ya ji rauni, sai dai harin ya yi barna sosai ga sansanin dake kusa da iyaka da Isra'ila.

Wani shaidar gani da ido ya ce, a jiya Alhamis, an harba makaman roka daga zirin Gaza zuwa kudancin Isra'ila domin mai da martani ga matakin Amurka na ayyana birnin Kudus a matsayin babban birnin Isra'ila.

Kawo yanzu dai, babu wanda ya dauki alhakin harba makaman rokar.(Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China