in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU: za a gudanar da zabuka kimanin 18 a Afirka a shekarar 2018
2017-12-08 10:51:07 cri
Kwamishinan kula da harkokin zaman lafiya da tsaro na kungiyar tarayyar Afirka Smail Chergui ya bayyana cewa, a kalla zabuka 18 a ake fatan shiryawa a nahiyar a shekarar 2018 idan Allah ya kai mu.

Smail Cherguyi wanda ya bayyana hakan yayin da ya ke jawabi a taron tuntuba na MDD da AU karo 11 game da magance aukuwar rigingimu, ya ce kungiyar AU za ta sanya ido kan wadannan zabuka da za a gudanar a shekarar 2018 yadda ta kamata.

Kwamishinan ya ce, duk da fargabar da ake, ana saran gudanar da galibin wadannan zabuka cikin lumana. A cewarsa, kungiyar tarayyar Afirka, za ta sanya ido kan zabukan da za a gudanar a kasashen Masar, Mali, Saliyo da Togo. Sauran sun hada da Guinea Bissau, Madagascar da Jamhuriyar demokirayar Congo da kuma Zimbabwe.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China