in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mistura: Tawagar gwamnatin Syria za ta halarci taron Geveva
2017-12-08 10:08:01 cri
Manzon musamman na MDD mai kula da batun Syria Staffan de Mistura ya bayyana cewa, a ranar Lahadi ne ake saran tawagar gwamnatin Syria a tattaunawar zaman lafiyar kasar za ta dawo birnin Geneva, bayan kauracewa zaman taron a wannan mako.

De Mistura ya ce, gwamnatin Syriar ta sanar da shi a jiya Alhamis cewa, tawagar za ta dawo birnin Geneve don shiga a dama da ita a tattaunawar, a kokarin da ake na samar da zaman lafiya, bayan da kasar ta shafe shekaru bakwai tana fama da mummunan tashi hankali.

Jami'in na MDD ya kuma shaidawa manema labarai a ofishin MDD dake Geneva cewa, ana ci gaba da tattaunwa da bangaren 'yan adawa, game da rubuta sabon kundin tsarin mulkin kasar da kuma zabukan da za a gudanar a kasar karkashin kulawar MDD, dukkan su ba tare da gindaya wasu sharudda ba.

A ranar 28 ga watan Nuwamba ne dai aka fara sabon zagayen tattaunawar zaman lafiyar Syriar da MDD ke jagoranta. Za kuma a ci gaba da gudanar da taron har zuwa ranar 15 ga watan Disamba a birnin Geneva.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China