in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jam'iyyar NCP ta Sudan na son karfafa alaka da jam'iyyar kwaminis ta Sin
2017-11-29 20:15:06 cri
Yau Laraba, mataimakin sakataren ofishin kula da harkokin Afirka ta jam'iyyar NCP dake kasar Sudan, Saifeelislam Omer Elimam, wanda a yanzu haka yake halartar taron karawa juna sani tsakanin jam'iyyun siyasun Sin da Afirka karo na uku a nan birnin Beijing, ya bayyana cewa, jam'iyyarsa na matukar son inganta alaka da jam'iyyar kwaminis ta Sin, a wani mataki na neman ci gaba tare.

Yayin da yake zantawa da wakiliyar CRI a yau, Saifeelislam Omer ya godewa jam'iyyar kwaminis ta Sin saboda goyon-bayan da ta dade take nuna mata, kana, jam'iyyar NCP ta Sudan na fatan yin amfani da wannan dama, domin kara koyon nasarorin da jam'iyyar kwaminis ta Sin ta samu a fannin tafiyar da mulkin kasa.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China