in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin ya sanar da samar da tallafin kudi ga hadin gwiwar CEEC
2017-11-27 20:31:15 cri
Firaministan kasar Sin Li Keqiang ya sanar da cewa, za a tallafawa hadin gwiwar kasashen Sin da da na yankin tsakiya da gabashin Turai 16 (CEEC) da kudade

Li wanda ya bayyana hakan yayin da yake gabatar da jawabi a taron dandalin tattalin arziki da cinikayya na Sin da kasashen tsakiya da gabashin Turai karo na bakwai a birnin Budapest na kasar Hungry, ya kuma sanar da kafa kungiyar hadin kan bankunan Sin da hadakar kungiyar kasashen na CEEC da kuma kashi da biyu da gidauniyar hadin gwiwar Sin da kasashen yankin tsakiya da gabashin Turai.

Mr Li ya ce bankin ci gaba na kasar Sin zai samar da kimanin euro biliyan biyu, kwatankwacin dala biliyan 2.4 a matsayin kudin rance ga kungiyar da aka kafa.

A halin da ake ciki kuma, firaministan na kasar Sin ya bayyana cewa, kashi na biyu na gidauniyar hadin gwiwar zuba jarin da za ta kai dala biliyan 1, za a zuba shi ne a yankin tsakiya da gabashin Turai.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China