in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Mugabe na Zimbabwe ya yi murabus
2017-11-22 10:15:04 cri
Shugaban kasar Zimbabwe Robert Mugabe ya yi murabus a jiya Talata. Shugaban majalisar dokokin kasar Jacob Mudenda ne ya sanar da Murabus din yayin zaman hadaka na majalisun dokokin kasar a jiya, inda suke muhawara kan tsige shugaban.

Wasikar murabus din ta ruwaito shugaba Mugabe na cewa, 'Ni Robert Gabriel Mugabe, bisa sashe na 96 karamin sashe na 1 na kundin tsarin mulkin Zimbabwe, ina mika murabus dina a hukumance a matsayin shugaban kasar Zimbabwe nan take'

Murabus din na zuwa ne kwanaki 2 bayan jam'iyyar Zanu PF mai mulkin kasar ta cire Mugabe a matsayin shugabanta tana mai kiran ya sauka daga mulkin kasar bisa jerin wasu tuhume-tuhume

Jam'iyyar ta nemi Mugabe ya yi murabus kafin karfe 12 na ranar Litinin, sai dai ya yi watsi da wa'adin, al'amarin da ya sa 'ya'yan majalisar dake majalisun dokoki su fara yunkurin tsige shi a jiya.

Sai dai, bayan fara yunkurin sai kawai Mugabe ya yi murabus, al'amarin da ya kawo karshen mulkin kusan shekaru 40 yana yi a Zimbabwe.(Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China