in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta baiwa UNICEF gudummawar dala miliyan biyu don taimakawa yara a Somaliya
2017-11-22 10:09:11 cri
A jiya Talata ne gwamnatin kasar Sin ta baiwa asusun tallafawa kananan yara na MDD(UNICEF) gudummawar tsabar kudi har dala miliyan biyu domin taimakawa kananan yara dake fama da karancin abinci mai gina jiki a yankunan kudanci da tsakiyar kasar Somaliya.

Da yake Karin haske yayin a Mogadishu, babban birnin kasar ta Somaliya jakadan kasar Sin a kasar Somaliya Qin Jian ya bayyana kudurin kasarsa na taimakawa matakan da Somaliya ke dauka na samar da kayayyakin jin kai da galibi kananan yara da mata ke matukar bukata.

Jakada Qian ya ce, kasar Sin na fatan hada kai da asusun na UNICEF don kaiwa ga al'ummomin dake wurare masu wahalar shiga kuma ke cikin mawuyacin hali. Ya ce za a yi amfani da kudaden ne wajen sayen abinci mai gina jiki da magunguna don baiwa mutanen dake cikin hadari, ciki har da yara 15,000 wadanda ke fama da matsalar karancin abinci mai gina jiki sakamakon matsalar farin da ake fama da ita a wasu sassan kasar.

Alkaluman asusun na UNICEF sun nuna cewa, kasar dake yankin kahon Afirka na fama da matsalar jin kai ne sakamakon kanfon ruwan sama, lamarin da ya tilastawa jama'a barin muhallansu, barkewar cututtuka da matsalar abinci mai gina jiki, inda a halin yanzu mutane miliyan 6.2 ke bukatar taimakon jin kai, kuma miliyan hudu daga cikin wannan adadi kananan yara ne.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China