Ziyarar jami'an diplomasiyya a lardin Jiangsu-An kammala ziyarar jami'an diplomasiyya a lardin Jiangsu
Kwanan nan ne jami'an diplomasiyya dake ziyara a lardin Jiangsu na kasar Sin suka kammala ziyarar da suka kai a lardin. A tsawon kwanaki shida da suka shafe suna wannan ziyara, jami'an diplomasiyyar da suka zo daga kasashe bakwai, ciki har da Mr.Sidibe Mohamadou Aboubakar, jami'in kula da harkokin watsa labarai a ofishin jakadancin jamhuriyar Nijer da ke kasar Sin da ma sauran jami'an diplomasiyya da suka zo daga kasashen Afghanistan da Brazil Cambodia da sauransu suka ziyarcia biraren Nanjing da Zhenjiang da kuma Taizhou dake lardin na Jiangsu, inda suka gane wa idonsu bunkasuwar lardin da dadadden tarihinsa da kuma wurare masu ni'ima. (Lubabatu)