in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Taron Apec na shekarar 2017
2017-11-23 16:03:11 cri

A kwanakin baya ne, aka rufe taron hadin gwiwar tattalin arziki tsakanin kasashen yankin Asiya da Fasifik (APEC) karo na 25 a birnin Da Nang na kasar Vietnam, taron da ke hallara shugabannin kungiyar a kowace shekara.

Taron na bana, shi ne na biyu da aka gudanar a kasar Vietnam, bayan wanda aka shirya a shekarar 2006. Wannan shi ne taro na farko da shugabannin kasashen Amurka da Koriya ta Kudu da jagorar yankin Hong Kong na kasar Sin da Firaministan New Zealand suka halarta tun bayan rantsar da su a kan mukamansu.

Manufar taron kungiyar wadda aka kafa a shekarar 1989, ita ce bunkasa harkokin cinikayya ba tare da wani shamaki ba a yankin. Haka kuma taron na bana ya amince a kara yin mu'amula da juna a wannan yanki tare da mayar da yankin a matsayin muhimmin yankin hadin gwiwar tattalin arzikin duniya, karfafa yankin cinikayya cikin 'yanci, samar da ci gaba mai dorewa ba tare da la'akari da wani bambance-bambance ba.

Sauran sun hada da taimakawa hukumomin cinikayya da kanana da matsakaitan masana'antu, samar da abinci da kuma uwa uba raya aikin gona.

Masana na cewa, taron wani dandali ne dake karfafa martaba dokokin cinikayya da yin takara da nuna daidaito tsakanin kasashe. (Ahmed, Saminu, Ibrahim/Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China