in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi girgizar kasa mai karfi a gundumar Milin dake jihar Xizang
2017-11-18 13:37:50 cri
Hukumar kula da harkokin girgizar kasa ta kasar Sin ta ce, ba tare da wani jinkiri ba, ta dauki matakan gaggawa domin tinkarar iftila'in girgizar kasa, tun bayan wadda ta auku mai karfin maki 6.9 a gundumar Milin ta birnin Nyingchi dake jihar Xizang.

Hukumar ta ce ta kira wani zaman taro na hoton bidiyo, inda ta kara fahimtar halin da ake ciki a wurin da bala'in ya auku, tare kuma da kiran kwararru daga hukumomin kula da harkokin girgizar kasa na lardunan Yunnan da Sichuan, don su taimakawa Xizang nazarin girgizar da ta auku a wannan karo, gami da wanda ka iya faruwa a nan gaba.

Su ma a nasu bangaren, wasu kwararru daga hukumar kula da harkokin girgizar kasa ta kasar Sin, wadanda a yanzu haka suke gudanar da ayyuka a yankin Xizang, sun garzaya zuwa yankin da biftila'in ya shafa, a wani kokari na taimakawa mahukuntan yankin gudanar da ayyukan shawo kansa. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China