A yau Talata ne kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Madam Hua Chunying, ta bayyana a nan birnin Beijing cewa, Sin na fatan za a cimma babbar nasara a yayin ziyarar da shugaban kasar Amurka Donald Trump zai kawo kasar Sin, a yunkurin kara bunkasa huldar da ke tsakanin kasashen biyu gaba.
Bisa goron gayyatar da shugaban kasar Sin ya ba shi, shugaba Trump zai fara ziyarar aiki a kasar Sin ne daga gobe 8 ga wata zuwa 10 ga watan nan, ziyarar da za ta kasance ta farko da kasar Sin ta karba, bayan babban taron wakilan jam'iyyar kwaminis mai mulki a kasar karo na 19.(Lubabatu)