in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban AU zai kai ziyara Sudan don tattauna halin da kasar ke ciki
2017-11-05 12:43:39 cri
Ma'aikatar harkokin wajen Sudan ta sanar da cewa shugaban kungiyar tarayyar Afrika (AU) Moussa Faki Mahamat, zai fara ziyarar aiki ta kwanaki 3 zuwa Khartoum daga ranar Lahadin nan, domin tattaunawa game da batutuwan da suka shafi kasar.

Sanarwar da ma'aikatar harkokin wajen Sudan din ta fitar ta bayyana cewa, shugaban na AU zai fara ziyarar tasa ne da tattauanwa da ministan harkokin wajen kasar Ibrahim Ghandour,.

A cewar sanarwar, tattauanwar jami'an zata mayar da hankali ne kan halin da ake ciki a kasar ta gabashin Afrika da kuma sauran batutuwa da suka shafi nahiyar Afrika.

Mahamat zai kuma gana da shugaban Sudan Omar al-Bashir da firaiministan kasar Bakri Hassan Saleh.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China