in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta zartar da kudurin da ya nemi Amurka ta soke takunkumin da ta garkamawa Cuba
2017-11-02 13:18:55 cri
Majalisar Dinkin Duniya ta zartas da wani kudiri da ya sake bukatar Amurka ta kawo karshen takunkumin da ta kakabawa kasar Cuba, a fannonin tattalin arziki, kasuwanci da kuma harkokin kudi.

Dukkanin kasashe membobin MDD 193 ne sun jefa kuri'un yayin babban taron MDD karo na 72, inda aka samu kuri'un amincewa guda 191, yayin da Amurka da Isra'ila suka jefa kuri'ar na ki. Wannan shi ne karo na 26 da aka zartas da irin wannan kudiri a wajen babban taron MDD.

Kudirin ya sake kira ga dukkanin kasashe, da kada su amince da wata doka ko matakan sanyawa kasar Cuba takunkumi, tare kuma da sake bukatar kasashen da har yanzu suke daukar irin wannan matakai da su soke tare da kawo karshensu.

Kasar Amurka ta dade tana jefa kuri'ar na ki game da kudirin soke takunkumin da aka sanyawa Cuba. A bara, yayin da ake samun kyautatuwar alaka tsakanin Amurka da Cuba, Amurka ta jefa kuri'ar janye jiki. Amma bayan Donald Trump ya dare kan karagar mulki, sai aka sake ci gaba da zaman doya da manja tsakanin kasashen biyu.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China