in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wasu shugabanni, da jam'iyyun siyasa da kungiyoyi na kasa da kasa sun taya kasar Sin murnar kira babban taron wakilan jam'iyyar kwaminis karo na 19
2017-10-24 13:23:25 cri
Yayin da ake gudanar da babban taron wakilai na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 19 a nan birnin Beijing, wasu shugabanni da jam'iyyun siyasa da kungiyoyi na kasashe daban-daban sun aiko da sakwanni ko kuma kira ta waya, domin taya Sin gagarumar murnar kiran taron.

A cikin sakon da ya aiko, jagoran al'ummar Falasdinawa Mahmoud Abbas, ya ce muhimmin rahoton da babban sakatare na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin Xi Jinping ya gabatar, ba ma kawai ya bayyana babban burin da al'ummar kasar Sin ke son cimmawa ba ne, wato farfado da al'ummar Sinawa, da raya kasa har ta zama kan gaba a duniya, har ma zai samar da alfanu ga daukacin al'ummar duniya. Abbas ya kara da cewa, gudanar da babban taron cikin nasara, ya kafa alkibla ga jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin, domin jagorantar ayyukan raya kasar Sin a nan gaba.

Sa'an nan a nasa bangaren, shugaban Jamhuriyar Kongo, Denis Sassou-Nguesso ya ce, jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin tana da wani babban buri na raya duniya mai adalci da wadata, kuma sakamakon matukar kokarin da ta yi, jam'iyyar kwaminis din ta raya kasar Sin har ta zama abar koyi ga duk duniya baki daya.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China