in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sanarwa: Za a nuna ganawar sabbin zaunannun membobin ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na JKS gobe
2017-10-24 11:05:10 cri
Gobe Laraba 25 ga wata ne, sabbin zaunannun membobin ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin za su gana da manema labarai a babban dakin taro na jama'a dake nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

A yayin ganawar, gidan rediyon kasar Sin CRI, zai watsa labarai game da bikin kai-tsaye cikin harsunan Sinanci, da Turanci, da kuma Rashanci. Baya ga kafar rediyo, za'a iya sauraren shirin ta kafar sadarwar zamani wato Internet, ciki har da shafin www.cri.cn na harsunan Sinanci, da Turanci da kuma Rashanci. Bugu da kari, za'a iya kama shirin ta manhanjar wayar salula ta CRI, wato ChinaRadio.

A dayan bangaren kuma, gidan rediyon CRI zai watsa shirin kai-tsaye cikin harsuna 40, ciki har da Hausa, da Sinanci, da Turanci, da Larabci, da Swahili, da Pashto, ta shafin sada zumunta na Internet, wadanda suka hada da Facebook, da Twitter, da WeChat, da Weibo, da manhanjar wayar salula ta ChinaNews, da ChinaTV da sauransu. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China