Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwar da Kakakin jihohin Oromia da Amhara suka wallafa a shafinsu na facebook game da tashin hankalin da aka shafe mako guda ana yi, wanda kuma ya haifar da cikas ga harkokin kasuwanci tare da kone-kone a wasu wurare daban-daban.
Kakakin Oromia Addisu Arega, ya ce a yanzu al'amura sun daidaita, kuma an kama mutanen da ake zargi da haddasa rikicin.
A nasa bangaren, kakakin Amhara Nigusu Tilahun cewa ya yi, rikicin ya raba mutanen da har yanzu ba a san adadinsu ba da muhallansu. (Fa'iza Mustapha)