in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministocin kasashen Afrika sun hadu a Rwanda domin tattauna yadda za a saukaka zirga-zirga a nahiyar
2017-10-21 12:56:15 cri
Ministocin kasashen Afrika sun hadu jiya Juma'a a Kigali babban birnin Rwanda, domin tattauna hanyoyin saukaka zirga-zirga a cikin nahiyar.

Taron na yini biyu zai tattauna yadda jama'a za su rika zirga-zirga cikin 'yanci da tsare-tsaren Tarayyar Afrika AU kan kaurar jama'a da kuma matakin da kasashen duniya suka cimma kan batun.

Taron wanda ke zuwa kwanaki 3 bayan wani taron masana kan batun, ya samu halartar ministocin kasashen nahiyar 30 wadanda ke kula da shige da fice.

Wani rahoton Bankin raya nahiyar Afrika ADB ya ce a shekarar 2016, mazauna nahiyar Afrika na bukatar visa kafin shiga kaso 54 cikin dari na sauran kasashen nahiyar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China