in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar sojin Nijeriya ta mika mayakan Boko Haram 760 ga Gwamnatin jihar Borno domin sake shigar da su al'umma
2017-10-07 12:19:18 cri
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta mika wasu mutane 760 da ake zargin 'ya'yan kungiyar Boko Haram ne ga Gwamnatin jihar Borno dake yankin arewa maso gabas domin sake shigar da su al'umma.

Wata sanarwa da kakakin rundunar sojin Col. Onyema Nwachukwu ya fitar a jiya Juma'a, ta ce an mika mutanen ne ga Gwamnatin jihar a cibiyar gyaran hali dake Unguwar Bulunkutu a Maiduguri babban birnin jihar.

Col. Onyema Nwachukwu ya ce an kama mutanen ne yayin aikin da dakarun rundunar Operation Lafiya Dole ke yi a yankin arewa maso gabashin kasar da nufin murkushe 'yan tada kayar baya, ya na mai cewa an kuma sallami mutanen ne bayan hadaddiyar cibiyar samar da bayanan sirri ta rundunar wato JIC, ta gudanar da bincike tare da yi musu tambayoyi.

Kakakin ya kara da cewa, Kwamadan cibiyar Brig-Janar Abdulrahman Kuliya ne ya mika mutanen ga Gwamnatin jihar.

Ya kuma yi kira ga al'umma su bada hadin kai tare da bada bayanai masu amfani ga hukumomin tsaro kan duk wani abu da ba su yarda da shi ba a yankunansu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China