in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijeriya ta tabbatar da nasarar da rundunar sojinta ta samu a yaki da Boko Haram
2017-10-07 12:04:06 cri
Gwamnatin Nijeriya ta ce rundunar sojin kasar ta samu gagarumar nasara a yaki da take da Boko Haram tun daga shekarar 2015.

Da yake jawabi yayin wani taro a birnin Fatakwal mai arzikin man fetur, babban hafsan sojin saman kasar Air Marshal Sadique Abubakar, ya ce rundunar sojin ta yi nasarar wanzar da zaman lafiya tare da tsare yankin arewa maso gabashin kasar daga ayyukan Boko Haram.

Air Marshal Abubakar, ya alakanta nasarorin da aka samu da farmaki ta sama da kasa da a ka kai kan tungar mayakan Boko Haram, tare kuma da kokarin sauran hukumomin tsaro.

Har ila yau, Babban hafsan sojin saman, ya ce rundunar sojin ta samu dimbin nasarori a yankin arewa maso gabas da sauran yankunan kasar tun bayan da sabuwar gwamnati ta kama aiki a shekarar 2015. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China