in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sarkin Sifaniya ya yiwa al'ummar kasar jawabi game da rikicin yankin Catalan
2017-10-04 12:20:02 cri
A jiya Talata ne Sarki Felipe na shida na kasar Sifaniya ya yiwa al'ummar kasar jawabi, kwanaki biyu bayan kuri'ar raba gardama da yankin Catalan ya kada, wadda kotun kundin tsarin mulkin kasar ta ce ya saba doka.

Jawabin sarkin na zuwa ne yayin da ake ci gaba da zaman dar-dar, yaje-yajen aiki da kuma bore a yankin Catalan, inda bayanan 'yan sanda ke cewa, mutane kimanin 300,000 sun bazama kan tituna don nuna rashin amincewarsu da matakan da 'yan sandan Sifaniya da dogarai masu tsaron jama'a suka dauka yayin kuri'ar raba gardamar ta ranar Lahadi.

Sarki Felipe ya dora alhakin tashin hankalin kan mahukuntan yankin na Catalan, yana mai nanata cewa, matakinsu na neman 'yancin kan yankin ya sabawa kundin tsarin mulki.

Ya ce, halayyar mahunkuntan yankin na rashin hankali, ta sanya tattalin arzikin Catalonia da ma Sifaniya baki cikin halin rashi tabbas. A saboda haka ya ce, a wannan hali da ake ciki, hakkin mahukuntan kasar ne su tabbatar da zaman lafiya a kasar.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China