in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Najeriya ya sha alwashin kakkabe rashawa a kasar
2017-10-02 12:49:02 cri
Yaki da rashawa a Najeriya kasar da tafi yawan jama'a a nahiyar Afrika, ba abu ne da za'a kammala shi cikin kankanin lokaci ba, inji shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.

A jawabin da ya gabatar wa al'ummar kasar a ranar Lahadi don bikin murnar cika shekaru 57 da samun 'yancin kasar a Abuja, babban birnin kasar, shugaba Buhari ya ce, gwamnatin tarayya ta tanadi tawagar masu bincike, kuma tana tattara dukkan sahihan bayanai wadanda zasu bada damar tuhumar jami'an gwamnati da aka samu da hannu wajen aikata rashawa.

Yace dama suna tsammanin wadanda suke da hannu a aikata rashawa zasu iya daukar dukkan matakai na mayar da martani a yakin da ake da rashawar, musamman ta hanyar yin amfani da bangaren shari'a don haifar da tarnaki da kuma yin amfani da siyasa. Sai dai a cewar shugaban, gwamnatinsa ta himmatu wajen kawar da rashawa daga tsarin siyasar kasar baki daya.

Shugaban Najeriyar yace, gwamnati ta samu nasarar kwato wasu daga cikin kudaden da aka sace cikin hanzari, ya kara da cewar, Najeriya ta sanya hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa da wasu aminan kasashen duniya game da sha'anin aikata munanan laifuka.

Buhari yace alamu sun nuna cewa ana samun karin hadin kai daga bangaren shari'ar kasar game da batun na yaki da rashawa.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China