in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za'a bude cibiyar watsa labarai ta babban taro na 19 na wakilan jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin
2017-09-29 14:52:30 cri
Za'a kaddamar da cibiyar watsa labarai ta babban taro karo na 19, na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin, a ranar 11 ga watan Oktoba dake tafe.

Cibiyar dai za ta iya kokarinta, wajen taimakawa manema labarai daga yankunan Hong Kong da Macau, gami da Taiwan, da na sauran kasashe, wajen samun katunan izinin watsa labarai. Wani aiki na daban da cibiyar za ta yi shi ne, gudanar da taron manema labarai, da samar da taimako ga manema labarai, don su samu damar bada rahotanni game da babban taron.

Har wa yau, cibiyar za ta bude tashar Intanet, da kuma wallafa bayanai ta kafar manhajar WeChat, domin samar da hidimar fasaha da bayanai ga manema labarai a yayin babban taron dake tafe a wata mai zuwa.

'Yan jaridun kasashen ketare za su iya tuntubar wasu lambobin waya don samun taimako, wato+861068576100, +861068576200, da kuma +861068576300. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China