in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zantawar wakilin sashin Hausa na CRI da gwamnan jihar Kano
2017-10-08 11:50:33 cri

A yau shirin zai kawo wa mai sauraro tsaraba ce daga taron hadin gwiwar raya masana'antu tsakanin wasu kasashen Afirka, da gwamnatin lardin Hunan dake nan kasar Sin, taron da ya gudana tsakanin ranekun Alhamis 21 zuwa Asabar 24 ga watan Satumba.

A yayin taron dai wakilai daga kasashen Najeriya, da Algeria, da Sudan ta Kudu da Losotho, sun saurari irin damammaki dake akwai na hadin gwiwar raya sassan masana'antu daban daban, ciki hadda na ayyukan gona, da samar da abababen more rayuwa, da na hakar ma'adanai da kuma samar da makamashi.

A bangaren Jihar Kano dake arewacin Najeriya, gwamnan jihar Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya jagoranci tawagar wasu jami'an gwamnatin sa, zuwa lardin na Hunan, inda suka saurari tanaje tanajen dake akwai na hadin gwiwa, sun kuma gana da wasu wakilan masana'antun samar da irin shuka mai inganci, da na sarrafa na'urori, da motocin aikin noma. Kaza lika tawagar ta jihar Kano ta isa lardin Shandong, inda ta rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwar gina wani yankin manasan'antun sarrafa tufafi a jihar ta Kano tare da kamfanin Ruyi Group.

Yayin da gwamnan na jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ke lardin Hunan, wakilin mu Saminu Alhassan ya samu zantawa da shi, inda ya fara da tambayar sa dalilin da ya sanya su ganin dacewar halartar taron na wannan karo.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China