in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Brundi ya yabawa sakamakon da aka samu na hadin kai tsakanin kasarsa da Sin
2017-09-23 13:50:04 cri
Jiya Juma'a, shugaban kasar Brundi Pierre Nkurunziza ya nuna yabo kan sakamakon da aka samu wajen hakikanin hadin kai tsakanin kasarsa da kasar Sin, kana ya bayyana dangantakar dake tsakanin kasashen biyu da cewa dangantaka ce da ta fi kyau da kasar Burundi ta kulla tare da kasashen duniya.

Nkurunziza, ya bayyana hakan ne a yayin da ya karbi takardar aiki daga sabon jakadan kasar Sin dake Brundi mista Li Changlin a fadar shugaban kasar, inda ya kara da cewa, kasarsa na fatan kara neman sabbin hanyoyi na hada kai tare da Sin, kana kasarsa na maraba da kamfanonin kasar Sin da su zo kasar Brundi don zuba jari, ya bayyana fatansa na kara ciyar da dangantakar dake tsakanin kasashen biyu gaba.

A nasa bangare, jakada Li ya nuna yabo kan nasarar da kasar Brundi ta samu wajen inganta zaman lafiya da tsaro, da inganta samun jituwar al'umma da raya tattalin arzikin kasa da dai sauransu, ya kuma bayyana cewa, yana son yin kokari tare da bangaren Brundi a cikin wa'adin aikinsa, don zurfafa dangantakar hadin kai ta samun moriyar juna a tsakanin Sin da Brundi.(Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China