in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An ceto sojojin Najeriya wadanda tsagerun Niger Delta suka yi garkuwa da su
2017-09-23 12:44:52 cri
A ranar Juma'a wata rundunar sojin hadin gwiwa ta samu nasarar ceto sojojin kasar Nijeriya biyu wadanda ake zargin mayakan tsagerun yankin Niger Delta ne suka damke su a ranar Litinin.

Major Ibrahim Abdullahi, shi ne mai Magana da yawun rundunar sojin, ya shedawa 'yan jaridu a Yenagoa babban birnin jahar Bayelsa mai arzikin mai cewa, bayan sojojin da aka ceto, an kuma ceto wasu fararen hula su 4 a lokacin da dakarun sojojin suka kaddamar da aikin sintiri.

Ya ce sakamakon barin wuta da rundunar sojin suka kaddamar an samu hasarar rayukan wasu daga cikin masu garkuwar yayin da wasu daga cikinsu suka tsere da raunukan harbin bindiga a jikinsu inda suka shiga cikin dazuka.

Abdullahi yace daga cikin kayayyakin da sojojin suka gano a sansanin tsagerun sun hada da wasu manyan bindigogi 3, da emtin kwanson alburusai guda 8 dauke da kokon kan mutane da wasu kasusuwa.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China