in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin waje na kasar Sin zai halarci taro game da batun nukiliyar Iran
2017-09-19 20:03:56 cri
Gobe Laraba ne ake saran ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi zai tashi zuwa birnin New York na Amurka don halartar taron ministoci game da nukiliyar kasar Iran.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang wanda ya bayyana hakan ga taron manema labarai, ya ce kasashen Iran, Amurka, Burtaniya, Sin, Rasha, Faransa da Jamus za su gana a hedkwatar MDD, inda ake saran za su tattauna yadda za a aiwatar da matakan da aka cimma(JCPOA) kana su ba da jagoranci a siyasance kan yadda za a aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma game da nukiliyar kasar ta Iran.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China