in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan kabilar Oromo 70,000 ne suka rasa mutsugunanasu sakamakon fadan kabilanci da ya barke a Habasha
2017-09-19 19:58:22 cri
Rahotanni daga kasar Habasha na cewa, sama da 'yan kabilar Oromo 70,000 dake zaune a jihar Somali na kasar Habasha ne suka rasa matsugunansu bayan da suka shafe mako guda ana gwabza fadan kabilanci tsakaninsu da 'yan kabilar Somali, lamarin da ya haddasa mutuwar wasu mutane, baya ga 'yan kabilar ta Somali kimanin 300 da suma fadan ya tilasta musu barin yankin na Oromia.

Da yake karin haske kan lamarin, minista a ofishin harkokin sadarwa na gwamnatin Habasha Negeri Lencho ya bayyana cewa, gwamnati ta kafa wata rundunar soja don taimakawa wadanda fadan ya rutsa da su.

Ya kara da cewa, duk da fadan da ya barke a jiya a kan iyakar Oromia da jihar Somali, har yanzu al'amura na tafiya yadda ya kamata a yankin.

Bayanai na nuna cewa, jihohin Oromia da Somali sun shafe kusan shekaru 20 suna fama da rikicin kan iyaka.

Ko da a makon da ya gabata sai da wani kazamin fada ya barke a kan iyakar Oromia da Somali, lamarin da ya rikide zuwa fadan kabilanci, inda har mutane da dama suka mutu kana dubban jama'a suka bar muhallansu.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China