in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta bukaci Japan da kada ta keta ka'idojin UNESCO game da matan da sojoji suka yi lalata da su
2017-09-18 20:15:14 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya bukaci kasar Japan da ta nuna halin sanin ya kamata wajen gabatar da takardun bayanai game da sanya matan da sojoji da suka yi lalata da su a matsayin daya daga cikin kayayyakin tarihi na UNESCO, maimakon yin barazanar kin biyan kudaden zama mambar hukumar ta UNESCO.

Takardar da sama da kungiyoyi 10 suka gabatarwa hukumar UNESCO daga kasar Sin,Koriya ta kudu da wasu kasashe da yankuna game da wadannan mata, zai nunawa duniya irin yadda aka gallaza musu a lokacin yaki, kana a tuna da tarihi, a kuma rungumi zaman lafiya da kare martabar dan-Adam, kamar yadda ya shaidawa taron maname labarai.

Ya ce hakkin kungiyoyin kasa da kasa ne su biya kudadensu na zama mamba a kan lokaci. Kasar Sin ta bukaci Japan da ta waiwayi barnar da ta aikata a baya, kana ta gyara kura-kuranta sannan ta daina wani kauce-kauce game da wannan takarda.

Mr. Lu Kang ya ce yadda aka rika sanya wadannan mata cikin wannan yanayi da karfi ko tilasta musu yin lalata,wani mummunan laifi da sojojin Japan suka aikata a lokacin yakin duniya na biyu. Kuma akwai kwararan shaidu dake tabbatar da hakan.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China