in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Sin da Rasha na neman kara hadin gwiwa a fannin masana'antu
2017-09-15 11:32:55 cri
Ministocin kasashen Sin da Rasha sun gudanar da wani taro a jiya Alhamis, inda suka tattauna kan yadda za su inganta hadin gwiwa a fannonin masana'antu da fasahohin zamani.

Yayin taron, ministan masana'antu da fasahar sadarwa na kasar Sin Miao Wei da ministan masana'antu da cinikayya na Rasha Denis Manturov, sun tattauna kan hadin gwiwa a fannonin da suka hada da sufurin jiragen sama da kayayyakin da ake sarrafawa da kayayyakin aiki da kuma kayan latroni.

Bayan tattaunawar, ministocin biyu sun kuma rattaba hannu kan yarjejeniyar jarin da kasar Sin za ta zuba a jamhuriyar Tatarstan na Rasha da kuma yarjejeniyar fahimtar juna ta gudanar da gasa kan kirkire-kirkire tsakanin Sin da Rasha.

Kusan wakilai 200 da suka hada da babban wakilin Sin a Kazan da 'yan kasuwa da malamai daga cibiyoyin ilimi na kasashen biyu ne suka halarci taron. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China