in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi baje kolin hotuna kan nasarorin da ta samu wajen kare hakkin dan Adam
2017-09-12 09:39:14 cri
An bude baje kolin hotuna mai taken 'domin kyautata rayuwar al'umma', a jiya Litinin a Hedkwatar MDD dake birnin Geneva na Switzerland, da nufin bayyana nasarorin da kasar Sin ta samu wajen inganta kare hakkin dan Adam a shekarun baya-bayan nan.

Baje kolin wanda shi ne irinsa na farko da aka taba yi a Hedkwatar majalisar, ya kunshi hotuna 70 da gajerun hotunan bidiyo 15, wadanda ke bayyana irin nasarorin da kasar Sin ta samu.

Wadanda suka yi kallon baje kolin sun hada da Jakadu da manyan jami'an diflomasiyya da jami'ai daga kasashe da hukumomin daban-daban tare da daruruwan wakilai dake halartar taro na 36 na hukumar kare hakkin dan Adam ta MDD. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China