in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
#BRICS# Shugaba Xi jinping ya ba da jawabi a yayin taron dandalin harkar masana'antu da cinikayya na kasashen BRICS
2017-09-03 18:52:28 cri

Da yammacin yau agogon kasar Sin ne aka bude taron dandalin harkar masana'antu da cinikayya na kasashen BRICS a birnin Xiamen, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da jawabi mai lakabi "A kokarta don inganta hadin kan kasashen BRICS cikin shekaru goma masu zuwa". Shekarar bana shekara ce ta cika shekaru 20 da kafuwar tsarin hadin kan kasashen BRICS, don haka taron dandalin harkar masana'antu da cinikayya na kasashen BRICS na bana ya jawo hankalin mutane sosai. A cikin jawabin da shugaba Xi Jinping ya gabatar, ya bayyana cewa, a cikin shekaru 10 da suka gabata, kasashen BRICS sun yi namijin kokari wajen neman bunkasuwa tare, sa'an nan sun inganta hadin gwiwar su don moriyar juna, baya ga sauke nauyi da ke wuyansu don ba da gudummowarsu ga fadin duniya.

Shugaba Xi ya jaddada cewa, hadin gwiwar kasashen BRICS na cikin wani muhimmin lokaci, wadanda ke fuskantar muhimman ayyukan da suka kunshi raya tattalin arziki da karfafa hadin gwiwa tsakaninsu. Ya ce ya kamata kasashen su kiyaye manufar hadin kan tattalin arziki, su kuma aiwatar da tsare-tsaren hadin gwiwa na kungiyar, tare da sa kaimi ga inganta tsarin hadin gwiwarsu daga dukkan fannoni.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China