in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ambaliyar ruwa ta yi barna a jihar Benue dake Nijeriya
2017-09-02 12:18:01 cri
Hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Benue SEMA, ta ce sama da mutane 100,000 ne ambaliyar ruwa ta shafa a yankuna 24 na jihar dake yankin tsakiyar Nijeriya.

Shugaban hukumar Boniface Ortese wanda ya bayyana haka a Makurdi babban birnin jihar, ya ce ambaliyar da ruwan sama kamar da bakin kwarya ya haifar ya shafi iyalai sama da 2,769.

Da yake ganewa idonsa barnar da ambaliyar ta yi a Makurdi da kewayenta, Gwamnan jihar Samuel Ortom, ya ce ibtila'in ya yi sanadin raba dubban mutane da matsugunansu a yankunan kananan hukumomi 12 na jihar.

Ya ce Gwamnatin jihar ta dauki matakan kare sake aukuwar ambaliyar da ta auku a jihar a shekarar 2012 inda ta rutsa da iyalai sama da 4,000 tare da sanadin mutuwar mutane da dama.

A nasa bangaren, shugaban kasar Muhammadu Buhari, ya umarci hukumar bada agajin gaggawa ta kasar NEMA, ta kai dauki ga mutanen da ambaliyar ta shafa a jihar Benue nan take. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China