in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hadin gwiwar Sin da jamhuriyar Benin zai fadada cin gajiya daga fannin yawon shakatawa
2017-09-01 20:40:57 cri
Wani babban jami'i a hukumar kula da harkokin yawon bude ido a jamhuriyar Benin, ya bayyana cewa fadadar hadin gwiwa da Sin, zai taimaka wajen bunkasa fannin yawon shakatawa a kasar.

Jami'in mai suna Jose Pliya, wanda ya zanta da kamfanin dillancin labarai na Xinhua, ya ce zurfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen 2, zai daga matsayin harkar yawon shakatawa a Benin. Ya ce kasar na da dama ta cin gajiya mai gwabi daga harkar yawon bude ido, to sai dai kuma ba a maida kai sosai wajen cin gajiyarsu ba.

Mr. Pliya na wannan tsokaci ne a gefen taron kasa da kasa game da harkar yawon bude ido da aka bude a birnin Kigali, fadar mulkin kasar Rwanda.

An dai bude taron na yini 4 ne a ranar Litinin, da nufin bunkasa harkar yawon shakatawa, harkar dake zama jigo ga bunkasar tattalin arziki, da samar da guraben ayyukan yi a daukacin sassan nahiyar Afirka.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China