in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Cikin shekaru hudu Sin ta cimma nasarar fidda mutane miliyan 13.9 daga kangin talauci
2017-08-29 20:47:27 cri
Wata sanarwa da majalisar gudanarwar kasar Sin ta fitar ta bayyana cewa, tsakanin shekarun 2012 zuwa 2016, adadin al'ummun kasar Sin wadanda suka samu kubuta daga kangin talauci ya kai mutum miliyan 13.91, yayin da yawan kudaden shigar mazauna karkara da ke fama da talauci ke karuwa da kaso 10.7 a duk shekara.

An dai gabatar da rahoton ne domin nazari, a yayin taron kwanaki 5 da kwamitin majalissar wakilan jama'ar kasar Sin NPC ke gudanarwa a watanni biyu biyu, taron da a wannan karo aka bude a ranar Litinin.

Rahotan ya shaida cewa, kasar Sin ta ayyana shekarar 2020, a matsayin wa'adin kammala gina al'umma mai wadata, matakin da ba zai tabbata ba har sai an cimma nasarar yaki da fatara.

Domin cimma wannan manufa, an bayyana cewa, Sin na bukatar fidda mutane miliyan 10 duk shekara daga kangin talauci, adadin dake nufi fitar da mutum miliyan daya duk wata, ko mutum guda 20 duk minti daya daga kangin talauci tsakanin al'ummar Sinawa. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China