in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamfanin kasar Sin zai kaddamar da layin dogon cikin birni a Nijeriya cikin Decemba
2017-08-23 12:40:59 cri
Kamfanin gine-gine na kasar Sin (CCECC) ya ce za a kaddamar da kashin farko na aikin shimfida layin dogon cikin birnin a Abujan Nijeriya cikin watan Decemba.

Manaja mai kula da aikin Kong Tao ya shaidawa manema labarai cewa, layin dogon wanda zai lakume dala miliyan 823 na da tsawon km 45 da kuma tashoshin daukar fasinja guda 12.

Hanyar za ta hada filin jirgin saman kasa da kasa na Nnamdi Azikwe da cibiyar hada-hadar kasuwanci ta birnin, yana mai cewa hanyar za ta kasance tagwaye.

Kong Tao ya kara da cewa, babban aikin na tafiya ba tare da tangarda ba.

A cewarsa, za a yi gwaji cikin watan Nuwamba sannan a kaddamar domin amfanin al'umma a watan Decemba.

Ya ce bayan kammala aikin, zai samar da ayyukan yi da bunkasa harkokin kasuwancin tare da habaka ci gaban tatalin arzikin kasar.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China