in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya zata sauya tunanin mayakan Boko Haram da suka mika wuya
2017-08-23 11:14:32 cri
Babban hafsan tsaron Najeriya Abayomi Olonisakin, yace gwamnatin kasar tana cigaba da daukar matakan sauya tunanin mayakan Boko Haram da suka mika wuya, gabanin basu damar shiga cikin al'umma don cigaba da rayuwa.

Jami'in ya bayyanawa manema labarai a Abuja babban birnin kasar cewa, gwamnatin Najeriyar tana yin kira ga magoya bayan kungiyar ta Boko Haram da su amince su mika wuya kuma su rungumi shirin zaman lafiya.

A cewar Olonisakin, babban abin da gwamnatin ta fi mayar da hankali kansa shine, sauya tunani, gyaran hali, da kuma sake maidowa tsoffin mayakan na Boko Haram tunaninsu domin su samu damar komawa hayyacinsu don cigaba da gudanar da rayuwar cikin alumma.

Yace a halin yanzu akwai tsaoffin mayakan 'yan tada kayar bayan su 96 a wani sansani dake jahar Gombe arewa maso gabashin kasar, kana akwai wasu mata da kananan yara su 565, wadanda zasu halarci shirin sauya tunanin na tsawon makonni 12.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China