in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zambia za ta karbi bakuncin taron matan Afirka
2017-08-23 10:44:10 cri
Kasar Zambia za ta karbi bakuncin taron kasa da kasa na yini 3 game da ilimin mata, karkashin jagorancin dandalin mata masana a fannin ilimi na nahiyar tare da hadin gwiwar ma'aikatar ilimin kasar.

Ana dai sa ran halartar wakilai kimanin 500, ciki hadda masu dakin shugabannin kasashen Malawi, da Mali da kuma Uganda, za kuma a nazarci hanyoyi da dabarun bunkasa ilimi tsakanin matasa, da inganta kwarewar su ta fuskar jagoranci, da cudanya tsakanin yankuna, da nahiyoyi, da ma mataki na kasa da kasa, musamman a fannin tattauna batutuwa ilimi da daidaiton jinsi. Daga karshe ana fatan hakan zai dace da manufar kungiyar AU game da ciyar da ilimi gaba, kamar yadda yake kunshe cikin ajandar ci gaban nahiyar ta 2063.

Wata sanarwa daga ofishin ministan ilimin kasar ta Zambia Dennis Wanchinga, ta bayyana taken taro na wannan karo da "yunkurin samar da daidaito a fannin ilimi a nahiyar Afirka". Cikin sanarwar Mr. Wanchinga ya bayyana tasirin wannan taro da zai gudana tsakanin ranekun 23 zuwa 25 ga watan nan da muke ciki, yana mai cewa dama ce ta duba dukkanin sassa na ciyar da ilimin mata da matasa gaba a nahiyar Afirka.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China