A taron manema labarai da aka kira a wannan rana a birnin Mogadishu, babban birnin kasar, Mukhtar Robow ya ce, yana fama da sabanin ra'ayi da sauran kusoshin kungiyar ta Al-Shabaab, kuma yana ganin cewa, abubuwan da kungiyar ke gudanarwa yanzu ba su dace da muradun jama'ar Somaliya ba, don haka, ya yanke shawarar fita kwata-kwata daga kungiyar. (Lubabatu)