in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin tsaron MDD da babban jami'in MDD sun yi Allah wadai da harin ta'addanci kan jami'an wanzar da zaman lafiya a Mali
2017-08-15 15:59:08 cri
Mambobin kwamitin tsaron MDD a ranar Litinin sun yi Allah wadai da babbar murya ga harin ta'addancin da aka kaddamar kan jami'an kiyaye zaman lafiya na MDD a Mali, wanda yayi sanadiyyar hallaka mutane 9.

Kwamitin tsaron MDDr ya bukaci gwamnatin kasar Mali da ta hanzarta bankado wadanda suke da hannu wajen kaddamar da harin, kuma ta gaggauta gurfanar dasu a gaban kotu.

Kwamitin tsaron MDDr ya bayyana harin da aka kaddamar kan jami'an wanzar da zaman lafiyar da cewa zai iya zama laifukan yaki ne karkashin dokokin kasa da kasa.

Sakatare janar na MDD Antonio Guterres, yayi Allah wadai da kaddamar da harin kan sansanin dakarun kiyaye zaman lafiyar a Mali.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China