Kasar Faransa da wasu kasashen Afrika 5 da suka hada da Burkina Faso, Chad, Mali, Mauritania da Nijer, a watan da ya wuce suka cimma matsaya na kaddamar da runduna ta musamman mai yaki da 'yan tada kayar baya masu tsattsauran ra'ayi a yankin Sahel. (Ahmad)