in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mai martaba sarkin Kano na son karfafa hadin-gwiwa da kamfanonin kasar Sin a fannonion saka tufafi da mulmula karafa
2017-08-15 10:36:30 cri
Jiya Litinin ne, mai martaba sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya ci gaba da ziyarar aikin da yake yi a birnin Shanghai dake gabashin kasar Sin, inda ya gana da manyan jami'an wasu kamfanonin kasar Sin guda biyu, wato kamfanin saka tufafi na Shangtex gami da kamfanin mulmula karafa mai suna Baowu. Mai martaba sarkin ya bayyana niyyarsa, ta habaka hadin-gwiwa da wadannan kamfanoni, tare da yin kira a gare su don su zuba jari a Najeriya, musamman a fannonin da suka shafi tufafi, wutar lantarki, ma'adinai da sauransu, don taimakawa rayuwar al'umma da raya tattalin arzikin tarayyar Najeriya.

Daga bisa wakilinmu Murtala Zhang ya zanta da mai martaba sarkin, ga cikakkiyar hirarsu.

Wakilinmu Murtala Zhang ke nan a zantarwarsu da mai martaba sarkin Kano Muhammadu Sanusi II. A yau Talata da yamma ne kuma, ake saran mai martaba sarkin Kano gami da 'yan tawagarsa za su iso nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin, zangonsu na karshe a ziyarar da suke a kasar Sin a wannan karo. Kana gobe Laraba, mai martaba sarkin Kano zai gana da wasu manyan jami'an gwamnatin kasar Sin, inda wakilinmu Murtala zai ci gaba da aiko mana da rahotanni da hirarraki game da wannan ziyara.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China