in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Sin da Nijeriya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna ta fuskar musayar labarai
2017-08-12 12:48:24 cri
Kasashen Sin da Nijeriya, sun rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna jiya Juma'a a Abuja, da nufin inganta huldar dake tsakaninsu ta fuskar musayar labarai da bayanai.

An rattaba hannu kan yarjejeniyar ne tsakanin ma'aikatar yada labarai da al'adu ta Nijeriya da kuma ofishin watsa labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin.

Ministan yada labarai da al'adu na Nijeriya Lai Mohammed wanda ya sa hannu a madadin kasarsa, ya ce yarjejeniyar muhimmin ci gaba ne ga huldar diflomasiyyar dake tsakanin Nijeriya da kasar Sin.

Lai Mohammed ya kara da cewa, yarjejeniyar za ta inganta kawance da hulda tsakanin hukumomin watsa labarai na kasashen biyu.

Da farko, mataimakin Daraktan ofishin yada labarai na Majalisar gudanarwar kasar Sin Guo Weimin, ya ce cimma yarjejeniyar ta bude wani sabon babi na dangantaka tsakanin kasashen biyu a fannin watsa labarai da al'adu.

Guo Weimin ya ce ma'aikatarsa za ta inganta yada labarai game da Nijeriya a kasar Sin, ya na mai kira ga Ministan na Nijeriya shi ma ya tabbatar da haka a kasarsa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China