Yau Jumma'a, mai martaba sarkin Kano Muhammadu Sanusi II ya kai ziyara shahararren kamfanin sadarwa na kasar Sin mai hedikwata a birnin Shenzhen, wato Huawei. Mai martaba sarkiya maida hankali sosai kan cigaban harkokin sadarwa na kamfanin Huawei, da yadda za'a yi amfani da harkokinsa don kyautata zaman rayuwar al'ummar Najeriya, musamman talakawan kasar. (Murtala)