Ya ce, bisa ga shirin bankin, nan da shekaru biyar masu zuwa, za a ware kimanin kashi biyu daga cikin uku na rancen kudaden da bankin ke samarwa ga bangaren raya muhimman ababen more rayuwa da za su taimaka ga samun dauwamammen ci gaba.
Ya kara da cewa, reshen bankin da za a bude a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta kudu a mako mai zuwa shi ne reshe na farko da bankin ya bude, wanda kuma zai taimaka wa bankin wajen aiwatar da shirye-shiryensa a nahiyar Afirka, ta yadda zai kasance kofar bankin na shiga nahiyar Afirka.(Lubabatu)