in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da suka mutu a girgizar kasar da ta aukuwa lardin Sichuan na kasar Sin ya kai 19
2017-08-09 21:10:52 cri
Rahotanni daga lardin Sichuan na kasar Sin na cewa, yawan mutanen da suka gamu da ajalinsu sanadiyyar girgizar kasa mai karfin maki 7.0 da ta aukuwa lardin a daren jiya Talata ya karu zuwa 19, kana wasu 247 sun jikkata yayin da mutane 40 kuma suka ji rauni mai tsannani.

Cibiyar kula da girgizar kasa ta kasar Sin ta bayyana cewa, girgizar kasar ta aukuwa yankin Jiuzhaigou ne da misalin karfe 9.19 na dare agogon kasar Sin, kuma zurfinta ya kai kilomita 20.

Mahukuntan kasar Sin dai sun yi kiran da a dauki dukkan matakan da suka dace na samar da agaji da aikin ceto ga wadanda lamarin ya shafa.

Ma'aikatan agaji na taimakawa masu yawon bude ido da suka makale a wurin yawon shakata mai korama da jama'a ke son ziyararta na Jiazhaigou. Yanzu haka hukumomin sun riga sun kwashe sama da masu yawon shakatawa 45,000, domin sake musu matsuguni.

Hedkwatar rage radadin girgizar kasa ta lardin ta bayyana cewa, sama da ma'aikata 800 ne suke karade kauyuka don neman wadanda suka makale sakamakon wannan bala'i.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China