in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Rasha sun yi alkawarin hadin gwiwa don tabbatar da tsaro
2017-07-27 11:27:14 cri
Kasashen Sin da Rasha sun amince zasu karfafa hanyoyin sadarwa da yin aiki tare domin tsara dabarun tabbatar da tsaro, bangarorin biyu sun cimma matsaya ne a lokacin gudanar da taron tuntuba game da sha'anin tsaro karo na 13 a ranar Laraba a birnin Beijing.

Dan majalisar zartaswar kasar Sin Yang Jiechi, da sakataren tsaron kasar Rasha Nikolai Patrushev ne suka jagoranci taron tuntubar.

An bayyana taron a matsayin mafi alfanu a tarihin dangantakar dake tsakanin kasashen biyu. Yang ya bukaci bangarorin biyu dasu kara zakulo dabarun da zasu tabbatar da samun fahimtar juna da amincewa da juna don yin aiki tare da juna da nufin tabbatar da cigaban sha'anin tsaro, da karfafa sauran al'amurra da suka shafi moriyar kasashen biyu.

A nasa bangaren Patrushev, ya bayyana cewa, karfafa huldar diplomasiyya tsakanin bangarorin biyu shine babban abin da Rashar take dauka da muhimmanci, kana yayi alkawari cewa kasar Rasha zata cigaba da yin hadin gwiwa da kasar Sin domin tsara dabarun tabbatar da tsaro da ma sauran batutuwa da suka shafi tafiyar da al'amurran kasa da kasa.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China