in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'an ceto a Nijeriya sun kammala aiki a ginin da ya rushe
2017-07-27 09:43:43 cri
Jami'an aikin ceto a Nijeriya, sun kammala aiki a wani gini mai hawa 4 da ya rushe ranar Talata da rana a jihar Lagos dake kudancin kasar, al'amarin da ya yi sanadin mutuwar mutane 8.

An yi nasarar ceto wasu mutane 15, ciki har da wani yaro dan shekara 11.

Kakakin hukumar bada agajin gaggawa ta yankin kudu maso yammacin Nijeriya NEMA Ibrahim Farinloye, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, kafafun yaron mai shakara 11 sun riga sun guntule a lokacin da aka ciro shi daga burbushin ginin.

An ceto yaron ne da sanyin safiyar jiya Laraba, sama da sa'o'i 12 bayan ginin ya rushe.

Tawagar masu ceton, da ta kunshi jami'an NEMA da na hukumomin tsaron jihar da hukumar bada agajin gaggawa ta jihar LASEMA sun kammala aiki a wajen, bayan sun kai matakin karshe na gini da misalin karfe 1:30 na rana agogon Nijeriya.

Masu ceto sun shafe tsawon daren ranar Talata suna ceton mutane da ginin ya rufta da su. Kuma an kai manya-manyan kayayyakin aiki domin gudanar da bincike cikin burbushin ginin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China