in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban Sufeton 'yan sandan Nijeriya ya bukaci a tsaurara hukunci kan masu satar mutane
2017-07-27 09:38:17 cri
Babban Sufeton 'yan sandan Nijeriya Ibrahim Idris, ya ce za a iya kawar da matsalar satar mutane a kasar ne kadai idan aka tsaurara matakan hukunta masu satar mutane.

Ibrahim Idris ya bayyana haka ne jiya a Abuja, fadar mulkin kasar, inda ya ce abun takaici ne, yadda masu satar mutane suka fi masu kishin kasa samun 'yanci a Nijeriya.

Ya ce har yanzu, ba a ga inda aka gurfanar tare da yanke hukuncin zaman gidan yari ga wadanda ake zargi da satar mutane ba.

Babban Sufeton wanda ya bayyana haka lokacin da yake jawabi ga shugabannin rundunonin 'yan sandan jihohin kasar, ya ce tsaurara hukunci kan masu satar mutane zai sa su kauracewa mummunar dabi'ar.

Matsalar satar Mutane ta zama ruwan dare a Nijeriya, inda har ya kai matakin da za a ce da wuya rana ta wuce, ba tare da samun labarin satar wani ba a sassan kasar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China