in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan sandan Masar sun hallaka 'yan kungiyar Muslim Brotherhook 8 a Fayoum
2017-07-24 13:45:15 cri
A ranar Lahadi 'yan sandan kasar Masar sun hallaka mayakan dake biyayya ga kungiyar 'yan uwa musulmi ta Muslim Brotherhood su 8, a lokacin musayar wuta a lardin Fayoum, in ji ma'aikatar cikin gidan kasar.

Sanarwar da ma'aikatar ta fitar ta bayyana cewa, 'yan sanda sun afkawa sansanin da Muslim Brotherhood suke horas da mayakansu masu alaka da Hasm, dake Fayoum wanda ke da tazarar kilomita 100 a kudu maso yammacin birnin Cairo.

'Yan sandan sun yi dirar mikiya a sansanin ne, bayan samun wasu muhimman bayanai dake nuna cewa kungiyar tana shirin kaddamar da hare haren ta'addanci a kasar.

Sanarwar ta kara da cewa, an hallaka 'yan ta'addan ne bayan da suka budewa 'yan sanda wuta suna kokarin afka musu.

A yan kwanakin nan 'yan sanda sun hallaka mayaka 22 a lardin Giza dake kusa da Cairo a Suez Canal dake birnin Ismailia. An yi amanna cewa kungiyar Hasm tana zaune ne a birnin Cairo, kuma tana da alaka da kungiyar Muslim Brotherhood, da kuma kungiya mai fafutukar kafa daular musulunci ta IS dake da sansaninta a zirin Sinai.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China