in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta alkawarta hadin gwiwa da kasar Tunisia game da shawarar ziri daya da hanya daya
2017-07-20 20:52:34 cri
Mataimakin shugaban kasar Sin Li Yuanchao, ya ce kasar sa za ta karfafa hadin gwiwa da Tunisia, karkashin shawarar ziri daya da hanya daya.

Mr. Li wanda ya bayyana hakan a Alhamis din nan, yayin ganawar sa da ministan harkokin wajen Tunisia Khemaies Jhinaoui wanda ke ziyarar aiki a nan kasar Sin.

Li ya ce ana maraba da shigar Tunisia wannan shawara, ya kuma yi fatan sassan biyu za su zurfafa hadin kai mai ma'ana, musamman karkashin lemar kungiyoyin hadin gwiwa, kamar dandalin Sin da kasashen larabawa, da kuma na Sin da Afirka, ta yadda za a daga dangantakar sassa daban daban zuwa wani sabon matsayi.

A nasa bangare, Mr. Jhinaoui ya ce bangaren Tunisia na da burin shiga wannan shawara ta ziri daya da hanya daya, tare da sauran shirye shirye na hadin gwiwa daga dukkanin sassa.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China